Posted by dpek on 2026-03-24 10:22:51 |
Share: Facebook | Twitter | Whatsapp | Linkedin Visits: 30
SABON SHIRI MAI TABBATAR DA MAKOMAR DALIBAI: An Kaddamar da Dikko Students’ Care Initiative a Katsina
Wani muhimmin shiri da ke da nufin sauya rayuwar ɗalibai da matasa a Jihar Katsina, mai suna Dikko Students’ Care Initiative, na shirin fara aiki a hukumance, inda ake sa ran zai buɗe sabbin ƙofofi na ilimi, jagoranci da damar aiki ga dubban ɗalibai.
A wani muhimmin zama da aka gudanar a jiya, Darakta Janar na shirin, Dakta Hafiz Ibrahim Ahmed, PhD, ya gana da Mai Bai wa Gwamna Shawara kan Harkokin Dalibai, Nuhu Nagake, domin tsara hanyoyin da za su tabbatar da aiwatar da shirin cikin nasara. Taron ya mayar da hankali kan samar da shawarwarin karatu, horar da shugabanci, da kuma hanyoyin da za su taimaka wa ɗalibai su samu damar aiki da dogaro da kai.
Shirin na zuwa ne a matsayin wani babban yunƙuri na gwamnatin Malam Dikko Umaru Radda na ƙara saka hannun jari a kan matasa, tare da rage matsalolin da ke hana ɗalibai cimma burinsu. Ana sa ran wannan tsari zai zama wata gada da za ta haɗa ɗalibai da damammakin da za su gina makomarsu mai kyau.
Mai Bai wa Gwamna Shawara kan Harkokin Dalibai, Nuhu Nagake, ya yabawa jajircewar Dakta Hafiz Ibrahim Ahmed wajen ganin an samar da wannan shiri, tare da miƙa godiya ta musamman ga Gwamnan Jihar Katsina bisa goyon bayan da ya bayar domin tabbatar da cewa matasan jihar sun samu ingantacciyar kulawa da jagoranci