Posted by dpek on 2026-03-24 08:27:44 |
Share: Facebook | Twitter | Whatsapp | Linkedin Visits: 20
Mai ba Gwamnan Jihar Katsina State shawara na musamman kan harkokin wutar lantarki da makamashi, Dr. Hafiz Ibrahim Ahmad, ya kaddamar da rabon tallafin jinkai ga al’ummar Kankia Local Government Area da kewayenta a ranar Lahadi, 8 ga March, 2026. An gudanar da wannan shiri ne a harabar sakatariyar karamar hukumar Kankia da misalin karfe 10:30 na safe.Shirin tallafin, wanda aka shirya ta hannun gidauniyar Ali CPC Development Foundation, ya zo ne domin taimakawa al’umma tare da karfafa hadin kai a yankin. Wadanda suka amfana sun hada da Limaman Sallar Idi na Kankia, mambobin Gwagware Foundation, kungiyoyin masu tuka okada,da Keke Napep, wasu da suka sauya sheka daga Peoples Democratic Party (PDP) zuwa All Progressives Congress (APC), da kuma sauran marasa galihu a cikin al’umma.Haka kuma, tawagar Dr. Hafiz da suka zo daga Katsina sun bayar da gudummawar naira miliyan daya domin a raba wa wadanda suka zo daga wurare masu nisa domin taimaka musu da kudin komawa garuruwansu.Wannan shiri na daga cikin kokarin gwamnati karkashin jagorancin Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, na tallafawa al’umma, taimakon masu karamin karfi, da kuma inganta hadin kai da walwalar rayuwar al’ummar Kankia.